Duk da sukar takarar Musulmai 2, an ga malaman coci a wurin kaddamar da Mataimakin Tinubu
A baya dai sun ce za su kauracewa bikin
Tinubu lokacin da yake kaddamar da Kashim Shettima
Mutane sun cika da mamaki bayan sun ga fuskokin malaman coci, ciki har da masu matsayin Bishop-Bishop a wajen kaddamar da Sanata Kashim Shettima a matsayin Mataimakin dan takarar Shugaban Kasa na APC, Bola Ahmed Tinubu.
Taron dai ya gudana ne ranar Alhamis a dandalin Shehu Musa ’Yar’aduwa da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.
- Ranar Alhamis masu gidajen burodin Najeriya za su fara yajin aiki
- An yi wa matashiya fyade sannan aka kashe ta a Edo
Tun da farko dai, kafafen yada labarai sun cika da labaran suka iri-iri daga kungiyoyin mabiya addinin Kirista daban-daban da ke sukar lamirin APC kan tsayar da Musulmai biyu a takarar.
Kungiyoyin dai sun yi ta kiran shugabanninsu da su kauracewa wajen kaddamar da mataimakin dan takarar don nuna bacin ransu a kai.
Ko a ’yan makonnin da suka gabata, sai da mai magana da yawun shugaban Kungiyar Kiristoci ta Kasa (CAN), Fasto Adebayo Oladeji ya yi Allah-wadai da matakin na APC.
A wani labarin kuma, Babban Sakataren CAN na kasa, Rabaran Joseph Bade Daramola, ya bayyana zabin Shettima a matsayin ayyana yaki da Kiristocin Najeriya.