EFCC ta cafke garin kudi na N11m a hannun masu sayen kuri’u

An kama wadanda ake zargin ne a wannan Asabar din yayin wani samame da aka yi ta hanyar leken asiri.

EFCC ta cafke garin kudi na N11m a hannun masu sayen kuri’u

Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) sun kama wasu mutane 14 da ake zargi da sayen kuri’u a rumfunan zabe a kananan hukumomin Otueke da Adawari da ke Bayelsa da kuma rumfunan zabe daban-daban a Imo da Kogi.

Mai magana da yawun EFCC, Dele Oyewale ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja.

A cewarsa, an kama wadanda ake zargin ne a wannan Asabar din yayin wani samame da aka yi ta hanyar leken asiri da aka fara kwanaki kadan gabanin zaben gwamnoni da ake gudanarwa a jihohin uku.

“Jami’anmu sun kwato jimillar tsabar kudi har N11,040,000, wanda suka kunshi N9,310,00 da aka kama daga hannun wadanda ake zargi da saye da sayar da kuri’u a Bayelsa.

“Akwai kuma N1,730,000 da aka kama daga hannun wadanda ake zargi da magudin zabe a Jihar Imo.

“Haka kuma an kama motoci biyu daga hannun wadanda ake zargin. Za a gurfanar da su gaban kotu da zarar an kammala bincike,” inji shi.

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan

A tabbatar an mutunta tsarin dimokuraɗiyya a Zaɓen Edo — Tinubu