El-Rufai ya bai wa Sarki Sanusi II mukami

Kwana daya da tube Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II daga gadon sarauta, Gwamnan jihar Kaduna Nasiru El-Rufai, ya ba shi mukami a Hukumar Fadada Zuba Jari ta Kaduna (KADIPA), inda ya zama mataimakin Hukumar. A cikin wata sanarwa da aka fitar daga gidan gwamnatin jihar Sir Kashim Ibrahim, wanda mai taimakawa Gwamnan kan watsa […]

El-Rufai ya bai wa Sarki Sanusi II mukami

Gwamna El Rufai da Malam Muhammadu Sanusi II

Kwana daya da tube Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II daga gadon sarauta, Gwamnan jihar Kaduna Nasiru El-Rufai, ya ba shi mukami a Hukumar Fadada Zuba Jari ta Kaduna (KADIPA), inda ya zama mataimakin Hukumar.

A cikin wata sanarwa da aka fitar daga gidan gwamnatin jihar Sir Kashim Ibrahim, wanda mai taimakawa Gwamnan kan watsa labarai ya rattaba hannu, mai suna Muyiwa Adekeye. A cikin sanarwar na bayyana cewa, mukamin da aka bai wa tsohon Sarkin nada alaka ne da kokarinsa wajen inganta tattalin arziki da kawo ci gaba a fannoni da dama a fadin duniya.

Sanarwar ta kara da cewa, wannan mukamin da aka bai wa Sanusi II a Hukumar KADIPA, Mataimakiyar Gwamnan jihar ce zata jagoranci masu gudanarwar Hukumar sai kuma wasu manyan jami’an gwamnatin jihar.