El-Rufai ya kai wa Obasanjo ziyara

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ziyarci tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo a Abeokuta, jihar Ogun a ranar Lahadi.

El-Rufai ya kai wa Obasanjo ziyara

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ziyarci tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo a Abeokuta, jihar Ogun a ranar Lahadi.

El-Rufai ya bayyana cewa ya ziyarci tsohon ubangidansa ne tare da abokansa, kimanin mako guda bayan da Sarkin Ijebu, Oba Sikiru Adetona ya nada El-Rufai a matsayin Gbobaniyi na kasar Ijebu.

Tsohon gwamnan ya ce “yau (Lahadi) na ziyarci maigidana, tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, tare da abokaina a gidansa na Abeokuta,” amma bai bayyana dalilin ziyarar ba.

A watan Satumba, El-Rufai ya bayyana Obasanjo a matsayin wanda ya fi kowa samun nasara ta fuskar bunkasar tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya.

ya bayyana haka ne a wani zama da aka yi a yayin taron Africa In the World a Afrika ta Kudu.

El-Rufai ya yi aiki a matsayin Darakta-Janar na Hukumar Kula da Kamfanonin Gwamnati (BPE) da kuma Ministan Babban Birnin Tarayya a gwamnatin Obasanjo na shekaru takwas.

An harbe ’yan sanda biyu a Yobe

Netanyahu ya bai wa Hamas wa’adin sakin Isra’ilawan da take garkuwa da su

Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman

‘Nijeriya ce ƙasa ta 140 mafi rashawa a Duniya’