El-Rufai Ya Kai Ziyara Sakatariyar Jam’iyyar SDP

Ziyarar tasa ta soma yamutsa hazo, inda wasu ke alakanta ta da siyasar 2027.

El-Rufai Ya Kai Ziyara Sakatariyar Jam’iyyar SDP

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya kai wata ziyara  sakatariyar jam’iyyar SDP ta kasa da ke Abuja, a ranar Laraba.

Ziyarar dai kawo yanzu babu wanda ya san gaskiyar dalilin ta.

SDP na daga cikin jam’iyyun da suka shiga zaben 2023, wanda El-Rufai ya taka muhimmiyar rawa a cikin jami’yyar APC da ta yi nasara a jiharsa ta Kaduna da kuma matakin Shugaban Kasa. 

Sunan Malam Nasiru na daga cikin wadanda aka mika wa majalisa domin tantnacewa a matsayin minista, sai dai bai samu sahalewar majalisar ba, sakamakon wasu dalilai da har yanzu ba a bayyana ba. 

Bayan wannan tirka-tirkace El-Rufa’i ya yi batan dabo a siyasa, inda  ba a kara jin duriyarsa ba a siyasance sai wannan ziyara da ya kai ofishin jam’iyyar SDP.

Ziyarar tasa ta soma yamutsa hazo, inda wasu ke alakanta ta da siyasar 2027.

Kotu ta tsige Ohinoyi na Ƙasar Ebira

Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba

HOTUNA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 4, shanu 15 da awaki 20 a Neja