#EndSARS: Kwamitin bincike ya dage zamansa
Kwamitin ya dage zamansa da mako guda bayan wata wakiliyar matasa ta kaurece masa.
Zauren Kwamitin Shari’a mai binciken dambarwar harbin Lekki a zanga-zangar #EndSARS a Jihar Legas
Kwamitin shari’ar binciken hatsaniyar zanga-zangar #EndSARS a Lekki, Jihar Legas ya dage zamansa zuwa ranar 14 ga watan Nuwamba.
Matakin na zuwa ne bayan daya daga cikin wakilan masu zanga-zangar #EndSARS a zaman Oluwarinu Oduala ta kaurace wa wa zaman a safiyar Asabar.
Oluwarinu Oduala ta ki halartar zaman ne saboda Babban Bankin Najeriya (CBN) ya rufe asusun bankin ta tare da na wasu jagororin zanga-zangar guda 18 bisa umarnin Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja.
Sakamakon haka, shugaban kwamitin, Mai Shari’a Doris Okuwobi (mai ritaya) ta sanar da dage ci gaban zaman zuwa ranar Asabar 14 ga Nuwamba, 2020.