Fasto ya je wa’azi coci da bindigar AK-47 a Abuja

Sai dai babu tabbacin ko bindigar na dauke da harsashi ko a’a

Fasto ya je wa’azi coci da bindigar AK-47 a Abuja

Wani Fasto mai suna Uche Aigbe da ya hau dandamalin coci da bindiga kirar AK-47 don yin wa’azi ranar Lahadi a Abuja ya jefa mabiyansa cikin rudani.

Faston dai ya dauko bindigar ne lokacin da yake takawa zuwa dandamalin da zai yi wa’azin, nan da nan kuma mabiyansa suka rude saboda rashin sanin abin da zai biyo baya.

Ganin hakan ne kuma ya sanya cikin barkwanci ya fara cewa ya zo ne da shirinsa saboda wasu mutane da ke neman shigar masa hanci da kudundune.

Ya kuma ce daukar bindiga a wannan lokacin ya zama wajibi, la’akari da yadda ake samun bara-gurbin Fasto-Fasto din da ke daidaita rayuwar mutane.

Sai dai babu wani rahoto da ya tabbatar da bindigar na dauke da harsashi ko a’a.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan