Ganduje, Tambuwal, Lalong da Ortom sun lashe zaben Gwamna
Gwamnonin jihohin Kano, Sakkwato, Filato da Benuwe sun lashe zaben rabar gardama da aka yi ranar 23 ga Maris 2019, yayin da jihohin Bauchi da Adamawa ke jiran umarnin kotu don sanin matsayar su. Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano da takwaransa na jihar Filato Simon Bako Lalong sun koma mukaminsu a kahro na biyu […]
Gwamnonin jihohin Kano, Sakkwato, Filato da Benuwe sun lashe zaben rabar gardama da aka yi ranar 23 ga Maris 2019, yayin da jihohin Bauchi da Adamawa ke jiran umarnin kotu don sanin matsayar su.
Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano da takwaransa na jihar Filato Simon Bako Lalong sun koma mukaminsu a kahro na biyu a jam’iyyar APC, inda Gwamnan Sakkwato Aminu Tambuwal da Gwamnan jihar Benuwe Samuel Ortom daga jam`iyyar adawa ta PDP suka lashe zaben.