Ganduje ya yi kira ga `yan takara su karbi kaddara
Gwamnan Jihar Kano Dokta Abdullahi Umar Ganduje ya yi kira ga `yan siyasa da su rungumi dukkanin hukuncin da suka samu a matsayin sakamakon zabe. Gandujen ya yi wannan kiran ne inda ya bayyana cewa, duba da yadda mutane suka fito don kada kuri’arsu, wannan ya nuna cewa dimokuradiyya ta samu zama a Najeriya. Gwamnan wanda […]
Gwamnan Jihar Kano Dokta Abdullahi Umar Ganduje ya yi kira ga `yan siyasa da su rungumi dukkanin hukuncin da suka samu a matsayin sakamakon zabe.
Gandujen ya yi wannan kiran ne inda ya bayyana cewa, duba da yadda mutane suka fito don kada kuri’arsu, wannan ya nuna cewa dimokuradiyya ta samu zama a Najeriya.
Gwamnan wanda ya sami rakiyar mai dakinsa Hajiya Hafsa Umar Ganduje ya kada kuri’arsa a mazabarsa ta Ganduje da misalin karfe 9:00 na safe.