Garuruwan da ake zargi da tu’ammali da naman jaki sun yi karin haske
Mahauta a garuruwan Jere da Sabo Wuse da Dikko da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna sun musanta zargin gasa naman jaki suna sanya alamar naman shanu ko na tumaki don yaudarar abokan huldarsu a garuruwansu. A makon jiya ne dai a babban labarin Aminiya, Sarkin Fawan Birnin Tarayya, Abuja, Alhaji Usman Datti, ya zargi […]
Mahauta a garuruwan Jere da Sabo Wuse da Dikko da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna sun musanta zargin gasa naman jaki suna sanya alamar naman shanu ko na tumaki don yaudarar abokan huldarsu a garuruwansu. A makon jiya ne dai a babban labarin Aminiya, Sarkin Fawan Birnin Tarayya, Abuja, Alhaji Usman Datti, ya zargi mahautan garuruwan da aikata almudahanar, zargin da shugabanninsu suka musanta.
A zantawarsa da wakilinmu Sarkin Fawan Jere, Malam kasimu Aliyu ya ce harkar fawa a garin Jere Musulmi ne ke gudanar da ita kuma ko a al’adarsu suna kyamar naman jaki. Malam kasimu Aliyu wanda ya nuna bacin ransa a kan al’amarin ya ce Sarkin Fawan Abuja wanda suke martabawa, kamata ya yi idan har ya fahimci ana haka a garin, sai ya sanar da su don su dauki mataki, saboda haka sun kalubalance shi ya nuna musu inda ake yanka jakuna ko gasa namansu a garin Jere, idan ya gaza hakan dole ya nemi gafarara ko su daukin matakin shari’a a kansa.
Sarkin Fawan ya dora ta’allaka zargin kan hassada game da bunkasar garin a harkar sayar da shanu saboda rugagen Fulani sun yi kewaye garin, kuma ya ce suna samun bunkasar cinikin danye nama da wanda ake gasawa bayan da aka bude sabuwar hanyar Bwari zuwa Jere da kuma aikin madatsar ruwa ta Gurara sannan ga tashar jirgin kasa da aka kaddamar a yanzu, “Mun tabbata za su ga haka kamar muna kwace musu ciniki ne,” inji shi.
Galadiman Fawan Sabon Wuse, Malam dan-Baba Muhammad da Sakataren Mahauta na garin Dikko Malam Tanko Sahabi sun musanta zargin sayar da naman jaki a yankunansu. Galadiman Fawan, ya ce masu sayar da naman jaki a garin kabilar Gwari ne ’yan asalin yankin wadanda suke sarrafa naman jaki a mashayar kasuwar garin a ranar da take ci. Ya ce wannan al’adarsu ce da suka same su a kai kuma har naman alade suke sarrafawa a wajen sai dai ya ce ba mahautansu a cikin harkar.
Galadiman ya ce a baya mutanen yankin na yanka jakin ne a wurin, amma kamar shekara 10 aka daina bayan sun nuna rashin yarda da hakan wanda sakamakon hakan yanzu suke kawo naman jakin daga kauyen Iddah duk ranar kasuwa su sayar da shi ga jama’arsu a bangaren mashayar.
Sakataren Mahautan Dikko wanda ya amince ana sayar da naman jaki a garin, ya ce ana yin haka ne a mashayar kasuwar a ranar Asabar da kasuwar garin ke ci. Ya ce lokacin da aka bude kasuwar, an so a hada su a wuri guda kamar yadda suke a tsohuwar kasuwar garin, amma sai suka ki amincewa. Ya ce masu mu’amala da naman jaki ba mahautansu ba ne wasu ne daga cikin ’yan asalin yankin.
Da aka sake tuntubar Sarkin Fawan Abuja Alhaji Usman Datti ya ce yana kan abin da ya ce kuma ba zai janye maganar ba. Alhaji Datti ya ce tuni wani jami’i da Ministan Abuja ya aika fadarsa ya tuntube shi a kan al’amarin da nufin daukar mataki a kan mahautar jakunan.