Gidaje da gonaki sun lalace sakamakon mamakon ruwan sama a Filato

Mutanen yankin sun nemi ɗauki daga gwamnatin jihar kan halin da suke ciki.

Gidaje da gonaki sun lalace sakamakon mamakon ruwan sama a Filato

Mamakon ruwan sama ya lalata gidaje sama da 20 tare da gonaki a yankin Darwat-Jol da ke Ƙaramar Hukumar Riyom a Jihar Filato, lamarin da ya tilasta wa jama’a da dama barin gidajensu.

Ruwan saman, wanda aka yi da yammacin ranar Asabar, ya haddasa ambaliya wadda ta mamaye yankin.

Wani mazaunin yankin, Malam Damba Dang, ya ce wannan na ɗaya daga cikin ruwan sama mafi ƙarfi da aka samu a yankin cikin a ‘yan shekarun nan.

Ya ce rashin ingantattun magudanan ruwa ne suka sa ambaliyar ta yi muni.

Ya ce gidaje da dama da aka gina da laka da ciyawa sun rushe, yayin da jama’a suka rasa kayan abinci, tufafi da sauran kayayyakinsu.

Mazauna yankin sun kuma ce ambaliyar ta lalata gonaki da dama, lamarin da ya ƙara jefa al’ummar da ke dogaro da noma cikin tsaka mai wuya.

Sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Filato, hukumomin agajin gaggawa da ƙungiyoyi da su kai musu agajin gaggawa domin tallafa wa waɗanda abin ya shafa.

Guguwa da ruwan sama sun yi ajalin mutum huɗu a Sakkwato

An kashe makiyaya uku a sabon hari a Filato

Kwale-kwale ya kife da mata da yara 40 a Jigawa

Sifaniya ta lashe Kofin Duniya na 2026