Gini mai hawa 3 ya rufta kan mutane a Legas
NEMA ta ce ba ta san adadin mutanen da ginin ya danne ba.
Wani gini mai hawa uku da ake ginawa ya rufta kan mutane a unguwar Yaba, da ke Jihar Legas.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ta ce ginin ya rufta ne da misalin ƙarfe 8 na dare.
- Gwamnatin Kuros Riba ta bankaɗo ma’aikatan bogi 800
- HOTUNA: Mahaifiyar Dangote ta halarci gasar karatun Alƙur’ani ta Shetty a Kano
Shaidu sun ce akwai mutane biyar zuwa shida a cikin ginin lokacin da abin ya faru.
NEMA ta ce ta ceto mutum huɗu, kuma an garzaya da su asibiti domin kula da lafiyarsu.
Sai dai hukumar ta ce ba a tabbatar da adadin waɗanda har yanzu suke ƙarƙashin ginin ba, yayin da ake ci gaba da aikin ceto.