Girgizar kasar Turkiyya: Yawan matattu ya haura 1,900
Wadanda suka rasu a Turkiyya sun kai 1,121 da wasu 810 a Syria baya ga wasu 783 sun jikkata.
Masu aikin ceto bayan girgizar kasar da aka samu a Turkiyya ta kashe daruruwa mutane a Syria. (Hoto: Can Erok/AFP)
Adadin mutanen da suka rasu a girgizar kasar da aka samu a kasar Turkiyya ya haura mutum 1,900 a kasar da kuma makwabciyarta, Syria.
Turkiyya sun ce wadanda suka rasu a kasar sun karu zuwa 1,121, a yayin da wasu 783 suka samu raunuka.
- Masu POS na cajin N3,000 kan kowace N10,000 da aka cire a wajensu a Anambra
- Karancin takardun kudi: Gwamnonin APC 3 sun maka Buhari a kotu
Hukumomin Syriya sun ce yawan mutanen da suka rasu a kasar sakamakon girgizar kasar ta safiyar Litinin ya karu zuwa sama da 810, wanda ya sa adadin haura mutum 1,900.
A safiyar Litinin ne aka samu girgizar kasar mai karfin maki 7.8, wadda aka ji ruguginta har a yankin Gaza da ke gaba da Syria aka ji.
Hukumomin ceto na ta kokarin ceto mutane da suka makale a cikin baraguzan gini da sauran wadanda lamarin ya shafa domin sama musu kayayyakin jin kai.