Gobara: An ceto mutum 6 da dukiyar miliyan 107 a Kano

Hukumar ta ja hankalin mutane kan kula da ababen amfani na gida.

Gobara: An ceto mutum 6 da dukiyar miliyan 107 a Kano

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta sanar da ceto rayukan mutum shida da dukiyar Naira miliyan 107 daga gobara 74 da suka faru a watan Fabrairun 2024, a jihar.

Kakakin hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi ne, ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN), a ranar Juma’a a Kano.

Abdullahi, ya kuma ce mutum hudu ne suka rasa rayukansu, yayin da gobarar ta kone dukiyar Naira miliyan 64.

“Mun samu kiran kai agaji bakwai daga kiran waya 10 daga mazauna jihar,” in ji shi.

Ya shawarci jama’a da suke kula sosai da abin da ya shafi wuta da lantarki.

Kazalika, ya ce wasu daga cikin gobarar sun tashi ne sanadin gas din girki.

Har wa yau, ya ce akwai bukatar mutanen jihar suke neman bayanai game da abin da ya shafi gobara da hanyoyin kare ta.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan