Gwamna da Sarkin Akure sun jajenta wa Hausawan da rikici ya rutsa da su

Kwana daya bayan rikicin Yarbawa da Hausawa na ranar Lahadin da ta wuce a garin Akure, Gwamna Rotimi Akeredelu na Jihar Ondo da Sarkin Akure Oba Ogunlade Aladelusi sun kai wata ziyarar gaugawa zuwa Unguwar Sabo inda Hausawan da aka yi rikicin  da mutum daya ya rasa ransa tare da asarar kadarori. Mataimakin Gwamna Mista […]

Gwamna da Sarkin Akure sun jajenta wa Hausawan da rikici ya rutsa da su

Kwana daya bayan rikicin Yarbawa da Hausawa na ranar Lahadin da ta wuce a garin Akure, Gwamna Rotimi Akeredelu na Jihar Ondo da Sarkin Akure Oba Ogunlade Aladelusi sun kai wata ziyarar gaugawa zuwa Unguwar Sabo inda Hausawan da aka yi rikicin  da mutum daya ya rasa ransa tare da asarar kadarori.

Mataimakin Gwamna Mista Agbola Ajayi ne ya wakilci Gwamnan a yayin da Oba Ogunlade Aladelusi ya jagoranci manyan fadawansa zuwa ganewa idanunsu irin barnar da aka yi da jajantawa wadanda al’amarin ya rutsa da su tare da yin kira ga bangarori biyu na Yarbawa da Hausawa su zauna lafiya da juna a unguwar ta Sabo/Odokoyi da irin haka bai taba aukuwa a baya ba.

Ziyarar shugabannin ta biyo bayan rade- radin ci gaba da fada ne a tsakanin bangagrorin biyu na Yarbawa da Hausawa a ranar Litinin da ta gabata bayan girke jami’an tsaro na sojoji da na ‘yan sanda da suka kwantar da rikicin na ranar Lahadi.

 Shi ma Kwamishinan ’yan sandan Jihar Ondo Mista Gbenga Adeyanju ya kai irin wannan ziyara inda ya tabbatar da cewa ’yan sanda sun dauki tsauraran matakan tsaro domin kwantar da rikicin tare da kafa kwamitin binciken da zai gano musabbabin tashin rikicin da kama dukkan wanda yake da hannu wajen haddasawa  domin hukumta shi.

Binciken da Aminiya ta gudanar ta gano cewa, an fara rikicin ne a ranar Lahadin da ta gabata a lokacin da wani ayarin dodannin Yarbawa suka ratsa ta Unguwar Hausawan a kan hanyarsu ta ziyartar sassa daban- daban na cikin gari domin gudanar da bukukuwan al’ada da suka saba yi a kowace shekara. Kamar yadda suka saba yi a al’adance mutum daya daga cikinsu ne yake lullube dukkan jikinsa suna rike da tsumangiya a hannayensu suna bin bayansa da rera wakoki da kade- kaden gargajiya

Binciken ya tabbatar da cewa, mabiya wannan dodo ne suka rika shada tsumangiya ga wasu Hausawa a wannan unguwa wanda suka fusata suka mayar da martani. “Wannan ne musabbabin rikicin da ya haifar da kone-konen gidaje da motoci da babura mallakar Hausawan” inji Mustapha Ali Imam jagoran matasan hausawan unguwar.

Jagoran matasan ya ce, “a gaskiya wadannan mutane (dodanni) sun sanar da shugabannin hausawa a game da ratsawa ta cikin unguwarmu wanda aka amince masu kamar yadda aka saba yi a kowace shekara. Sai dai a bana al’amarin ya canza salo a inda suka rika tsula wa jama’a bulala. Hakan ne ya sa matasan hausawan suka maida martani wanda ya kai ga tashin rikicin.”

Da yake yi wa jama’arsa (hausawa) jawabi, Sarkin Hausawan Akure Alhaji Babangida Sadik Kusada ya roke su ne su ci gaba da girmama doka da oda da kyautata zamantakewa tsakaninsu da mutanen gari kamar yadda suke yi a baya domin samar da zaman lafiya mai dorewa a Jihar Ondo da ma a kasa baki daya.

Sarkin Hausawan ya nuna matukar farin cikinsa da hanzarta kawo dauki da Gwamna Rotimi Akeredelu da Oba Ogunlade Aladelusi suka kai wa hausawan. Ya ce, “a yau Talata ma wasu sarakuna da hakimai da shugabannin kungiyoyi dukkansu Yarbawa sun kawo irin wannan ziyara domin jajenta mana.”

Ya ce, “wannan al’amari tsautsayi ne domin muna zaune lafiya a tsakaninmu da mutanen gari ba mu taba ganin irin haka a shekarun baya ba. Ina tabbatar maka cewa yanzu jama’armu sun fito suna ci gaba da gudanar da harkokinsu lami lafiya.”

Wata majiya daga ofishin Gwamnan ta yi wa Aminiya bayanin cewa Gwamna Akeredelu bai ji dadin aukuwar al’amarin ba. Har ma ya fara duba yiwuwar biyan diyya ga wadanda suka yi asarar kadarorinsu a yayin rikicin.