Gwamna Fashola ya bukaci a kirkiro ’yan sandan jiha
Tabarbarewar harkokin tsaron da Najeriya ke fama da shi yasa bukatar samar da ’yan sandar jiha ta zama wajibi, domin tallafa wa tsaro a cikin kasa, idan ba haka ko lamarin ya ci gaba da sukurkucewa, a cewar Gwamnan jihar Legas Mista Babatunde Raji Fashola.Gwamnan ya yi wannan kalamin ne a karshen taron ’yan majilisar […]
Tabarbarewar harkokin tsaron da Najeriya ke fama da shi yasa bukatar samar da ’yan sandar jiha ta zama wajibi, domin tallafa wa tsaro a cikin kasa, idan ba haka ko lamarin ya ci gaba da sukurkucewa, a cewar Gwamnan jihar Legas Mista Babatunde Raji Fashola.
Gwamnan ya yi wannan kalamin ne a karshen taron ’yan majilisar dokokin jihars da suka yi da bangaren zartaswa na jihar, domin musayar ra’ayi game da yadda za su ci gaba da tafiyar da ayyukan su ba tare da fuskantar matsala ba. Kuma sun kara fahimtar juna ta sanin ina suka fito, ina suka dosa.
Ya ce idan dai zai iya tuna abin da dokar kasa ta ce game da samar da ’yan sanda, yasan cewa ba inda aka yi hani da samar da ’yan sandar jiha. Domin a cewarsa, sai an samu hadin gwiwa ne tsakanin masu gudanar da mulki sa’ilin ne za a samu sauki a kome aka kudiri aniyar gudanarwa.
Gwamnan ya yi kira ga majalisun kasar nan guda biyu, da su sake duba wannan batu da idon basira, kuma su fitar da son rai ciki, domin samar da dokar kasa da za ta bada damar kirkiro da ’yan sandan jiha, wanda ya ce zai taimaka matuka gaya wajen tsaron.
Shi kuwa mai baiwa gwamna shawara a harkokin majilisa, Folami Muslim Oloruntele, cewa ya yi, makasudin wannan taron, shi ne, a yi musayar ra’ayi tsakanin bangaren mulki da masu yin dokoki, ta yadda zai amfani jama’ar jihar da ma kasa baki daya.