Gwamnan Bauchi ya jagoranci Sallar rokon ruwa

Kusan mako daya ke nan ana shirya rokon ruwan a Jihar

Gwamnan Bauchi ya jagoranci Sallar rokon ruwa

Gwamnana Jihar Bauchi, Bala Mohammed, a ranar Alhamis ya jagoranci dimbin jama’a domin yin Sallar rokon ruwa saboda karancin ruwan saman da Jihar ke fsukanta.

Jim kadan bayan idar da sallar, Gwamnan ya ce Jihar na fama da matsanancin fari yayin da damina ta lula, inda ya ce ya zama wajibi a yi sallar don neman taimakon Allah.

Ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da addu’ar domin manoma su sami damina mai albarka ta yadda za su sami amfani mai yawa.

Gwamnan, wanda ya samu wakilcin Mataimakinsa, Auwal Jatau, ya kuma gode wa Sarkin Bauchi, Alhaji Rilwanu Sulaiman Adamu da sauran malaman Jihar saboda shirya sallar.

Bala Mohammed ya kuma bukaci jama’ar Jihar da su goyi bayan manufofin gwamnatinsa, inda ya ce sun samar wa manoma takin zamani da sauran kayayyakin amfanin gona.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya rawaito cewa kusan tsawon mako guda ke nan, shugabannin al’umma da na addini suna shirya rokon ruwan domin neman agajin Ubangiji.

Mataimakin Babban Limamin Babban Masallacin Bauchi, Ahmad Auwal Na’ibi. (NAN)

’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo

Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano

Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad

Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC