Gwamnan Neja ya rushe kwamishinoninsa

Gwamna Mohammed Umaru Bago na Jihar Neja ya rushe majalisar kwamishinoninsa.

Gwamnan Neja ya rushe kwamishinoninsa

Gwamna Mohammed Umaru Bago na Jihar Neja ya rushe majalisar kwamishinoninsa.

Sakataren Yaɗa Labarai na gwamnan, Bologi Ibrahim, ya ce gwamnan ya sanar da rushe majalisar kwamishinoninsa ne a yayin taron Majalisar Zartarwa ta jihar a safiyar Litinin ɗin nan.

Ya kuma yaba musu bisa gudunmawar da suka bayar wajen kawo ci-gaba mai ma’ana a jihar tare da yi musu fatan alheri.

Sai dai kuma gwamnan ya sake nada sakataren gwamnatin da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati da mataimakinsa a da wasu jami’ai a kan muƙamansu.