Gwamnati kaɗai ba za ta iya ɗaukar nauyin Ilimi ba — Minista

Ya buƙaci masu hannu da shuni shigo cikin harkar domin tallafa wa ilimi kai-tsaye.

Gwamnati kaɗai ba za ta iya ɗaukar nauyin Ilimi ba — Minista

Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman, ya ce Gwamnatin Tarayya ita kaɗai ba za ta iya ɗaukar nauyin ilimi ba.

Ya bayyana hakan ne yayin wani taron karrama Dakta Emeka Offor da matarsa, Dokta Adaora Offor da Jami’ar Nsukka ta Najeriya (UNN) da jami’ar Nnamdi Azikiwe (NAU) Awka suka bai wa lambar yabo a fannin kasuwanci a Abuja.

Ministan, ya ce duk da cewa gwamnati ta kashe maƙudan kuɗaɗe wajen bayar da tallafin karatu, amma akwai buƙatar masu hannu da shuni su yi koyi da abin da Mista Offor da matarsa ​​suka yi wajen tallafa wa ilimi.

“An ƙarfafa ma’aikatar da irin wannan karramawa saboda gwamnati ba za ta iya ɗaukar nauyin ilimi ita kaɗai ba; kamar yadda ya bayar da gudunmawa mai yawa.

“Don haka ne mutane irin su Emeka Offor da matarsa ​​suka shigo ciki, kuma abin da suke yi ya kamata wasu su ƙarfafa masa gwiwa.

“Na yi imanin wannan kyakkyawan misali ne na albarkatun da aka yi amfani da su sosai, kuma ina kira ga wasu da su yi la’akari da abin da suka yi.”

Yayin da Jami’ar UNN ta karɓi Naira miliyan 100 don ayyukan bincike da masana’antar masana da za su yi tasiri a Tsangayar Kasuwanci ta Jami’ar.

Jamia’r NAU ta karɓi Naira miliyan 50 don taimakon zawarawa, yara masu buƙatu na musamman da sauran mabuƙata.

Waɗanda aka karrama kuma sun  bayar da tallafin, Cif Offor, ya ce asusun bayar da tallafi zai kasance taƙaitacce ne, inda za a gudanar da bayar da kuɗaɗen har abada sai dai wanda gidauniyar Sir Emeka Offor (SEOF) da jami’o’i suka yanke.