Gwamnati ta raba wa mata masu karamin karfi 15 injin niƙa a Edo

Ma’aikatar noma ce ta raba tallafi kyauta

Gwamnati ta raba wa mata masu karamin karfi 15 injin niƙa a Edo

Nasiru isiyaka yana kokarin tayar da injin nika.

Gwamnatin Tarayya ta raba wa wasu mata masu karamin karfi su 15 tallafin injin niƙa a Jihar Edo.

Ma’aikatar Ayyukan Gona da Samar da Abinci ta kasa ce ta raba kayan a wani mataki na wadata kasa da abinci.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) an ba kowacce daga cikin mata 15 din kyautar injin nika guda daya.

Babban Jami’i a ma’aikatar, Peter Pindar, ya ce an raba kayan ne karkashin shirin samar da tallafi ga mata da matasa kan hanyoyin sarrafa doya da adana ta domin ci gaban kasa.

A cewar Peter, ma’aikatar ta sayo injinan ne domin raba su ga mata a wani mataki na karfafa musu gwiwa. (NAN)

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan