Gwamnati ta raba wa mata masu karamin karfi 15 injin niƙa a Edo

Ma’aikatar noma ce ta raba tallafi kyauta

Gwamnati ta raba wa mata masu karamin karfi 15 injin niƙa a Edo

Nasiru isiyaka yana kokarin tayar da injin nika.

Gwamnatin Tarayya ta raba wa wasu mata masu karamin karfi su 15 tallafin injin niƙa a Jihar Edo.

Ma’aikatar Ayyukan Gona da Samar da Abinci ta kasa ce ta raba kayan a wani mataki na wadata kasa da abinci.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) an ba kowacce daga cikin mata 15 din kyautar injin nika guda daya.

Babban Jami’i a ma’aikatar, Peter Pindar, ya ce an raba kayan ne karkashin shirin samar da tallafi ga mata da matasa kan hanyoyin sarrafa doya da adana ta domin ci gaban kasa.

A cewar Peter, ma’aikatar ta sayo injinan ne domin raba su ga mata a wani mataki na karfafa musu gwiwa. (NAN)

Abin da ya sa na yi wa Buhari juyin mulki —Babangida

Yadda aka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga

Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi kan shan mangwaro a makaranta

NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri