Gwamnati za ta bai wa ma’aikata tallafin rage raɗaɗi a Yobe

Za a raba wa ma’aikatan Jihar Yobe Naira dubu talatin da biyar-biyar domin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur.

Gwamnati za ta bai wa ma’aikata tallafin rage raɗaɗi a Yobe

Gwamnan Jihar yobe, Maimala Buni

Gwamna Mai Mala Buni ya amince a raba wa ma’aikata N35,000 a matsayin tallafin rage raɗaɗin tsadar rayuwa a faɗin Jihar Yobe.

Wannan dai na zuwa ne a matsayin wani yunkuri da gwamnatin jihar ta yi na kawo wa ma’aikatan sauƙi sakamakon cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi tun a bara.

Sanarwar na ƙunshe ne cikin wata takarda da mukaddashin Shugaban Ma’aikatan Jihar Yobe, Hamidu M. Alhaji ya gabatar wa Sakataren Gwamnatin jihar, Baba Malam Wali a ranar Juma’ar da ta gabata.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, a bayan nan ne Gwamna Buni ya naɗa Sakataren Gwamnatin jihar a matsayin jagoran kwamitin mai mutum shida da zai jibinci al’amuran rabon tallafin na Naira 35,000 a tsakanin ma’aikatan jihar.

Bayanai sun ce an dora wa kwamitin alhakin tantance abin da ya shafi rabon kuɗin da kuma neman shawarwarin kungiyoyin kwadago kan kuɗaɗen da za a amince da su a matsayin tallafi daga bangaren gwamnati.

An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

‘A sansanin gudun hijira na yi sakandare har na zama likita’

An dawo da wutar lantarki a Kaduna

An kashe ɗan banga da yin garkuwa da ’yan mata 6 a Neja