…Gwamnatin Buhari ta gaza – Shekarau Ya ce ya bar Rarara da Allah

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Ministan Ilimi a zamanin gwamnatin Goodluck Jonathan Malam Ibrahim Shekarau ya ce gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta gaza wajen kyautata rayuwar al’ummar Najeriya kamar yadda take ikirarin za ta yi.Malam Ibrahim Shekarau ya bayyana haka ne lokacin da yake tsokaci a wajen wani taro da matasan Jam’iyyar PDP suka […]

…Gwamnatin Buhari ta gaza – Shekarau Ya ce ya bar Rarara da Allah
…Gwamnatin Buhari ta gaza – Shekarau Ya ce ya bar Rarara da Allah

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Ministan Ilimi a zamanin gwamnatin Goodluck Jonathan Malam Ibrahim Shekarau ya ce gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta gaza wajen kyautata rayuwar al’ummar Najeriya kamar yadda take ikirarin za ta yi.
Malam Ibrahim Shekarau ya bayyana haka ne lokacin da yake tsokaci a wajen wani taro da matasan Jam’iyyar PDP suka shirya mai taken  “Kowa ya tuna bara, bai ji dadin bana ba,” inda ya kara da cewa shekara guda ke nan da wannan gwamnati ta kama mulki amma har yanzu ’yan Nijeriya ba su samu saukin rayuwa ba kuma a cewarsa, babu  wani abu da ya canja.
Malam Ibrahim Shekarau ya ce “Mun gaya wa ’yan Najeriya cewa wannan gwamnati ta Jam’iyyar APC ba za ta iya komai ba, kuma ba za ta ceto al’umma daga halin da suke ciki ba, don haka har yanzu ake cikin wani hali a kasa na rashin jin dadin zamantakewa walau a birane ko kuma yankunan karkara.”
Tsohon Gwamnan ya yaba wa magoya bayansa da suke tare da shi a tafiya irin ta siyasa, tare da fatan za su ci gaba da goyon bayan jam’iyyarsu ta PDP wadda take da kyawawan tanadi ga jama’a.
A wani labarin Malam Ibrahim Shekarau ya ce ya bar fitaccen mawakin siyasar nan Dauda Kahutu Rarara da Allah kan fitar da wakar siyasar nan, mai taken “Malam ya ci kudin makamai.”
Malam Shekarau ya bayyana haka ne ta bakin kakakinsa Alhaji Ghali Sadik, inda ya yi kira ga magoya bayansa su yi hakuri kamar yadda suka saba, “Masu yunkurin zuwa kotu su yi hakuri ku bar shi da Allah. Hakuri shi ne halin Manzon Allah (SAW), duk mai yin sa ba zai yi nadama ba, haka kuma nasara na tare da shi,” inji shi.
Bayan fitowar wakar wacce ke cike da zambo da ake ganin an yi ta ne ga tsohon Gwamnan, magoya bayan Malam Shekarau a karkashin kungiyar Sardaunan Kano bisa jagorancin Sardaunan Matasan Rijiyar Lemo Sani Musa Muhammad suka bukaci Rarara ya fito ta kafafen watsa labarai ya janye kalamansa tare da neman afuwar tsohon Gwamnan, idan ba haka ba su dauki matakin shari’a a kansa.