Gwamnatin Jihar Legas na feshin yakar zazzabin cizon sauro
Mutanen da yawansu ya kai miliyan 3 da rabi ne gwamnatin Jihar Legas ta yi nasarar yi wa feshi a yankinsu don samun kariya daga zazzabin cizon sauro a shekarar da ta gabata, a karkashin shirin feshin maganin kwari da ta gudanar gida-gida. Kwamishinan kiwon lafiya na jihar, Dokta Jide Idris shi ne ya bayyana […]

Mutanen da yawansu ya kai miliyan 3 da rabi ne gwamnatin Jihar Legas ta yi nasarar yi wa feshi a yankinsu don samun kariya daga zazzabin cizon sauro a shekarar da ta gabata, a karkashin shirin feshin maganin kwari da ta gudanar gida-gida.
Kwamishinan kiwon lafiya na jihar, Dokta Jide Idris shi ne ya bayyana hakan sa’ilin da yake wa taron manema labarai jawabi jim kadan kafin a fara wani sabon shirin feshin na gida-gida.
Dokta Idris ya ce a bara an yi feshin ne a kananan hukumomi 13. Daga shekarar 2001 ce dai aka fara wannan shirin, wanda gidaje 49,003 suka amfana. Akan yi feshin ne a bangwaye da kuma cikin rufin daki inda sauro da sauran kwari ke makalewa domin kashe su kuma a hana su yaduwa.
Kwamishinan ya ce gwamnati ta samar da shirin ne domin rage yawan yaduwar sauro, lamarin da zai sa a rage yawan kamuwa da zazzabin cizon sauro, domin ba Jihar Legas ba, a daukacin Najeriya, cizon sauro ya zame barazana ga jama’a, shi ya sa gwamnati tabullo da shirin kuma ana samun nasara bakin gwargwadon hali.
Dokta Idris ya ce wannan shekarar za a yi a kananan hukumomi 6 da kuma duk yankunan raya karkara da suka fada cikin wadannan kananan hukumomin, kodayake za a mayar da hanklali a kananan hukumomin Ikorodu da Ibeju Kekki saboda bincike ya nuna su ne suka fi yawan samun barazanar cizon sauro idan an kwatanta su da auran.
Kwamishinan ya ce shirin yana cikin shawarwarin da hukumar lafiya ta duniya ta bayar kuma gwamnatin Jihar Legas ce kawai ta fara aiwatar da shi a Najeriya, saboda haka ne ma ya yi kira ga magidanta su hada kai da masu aikin feshin, musamman ta fuskar lullube kowane abinci ko na sha da kyau.
Ana sa ran za a yi kwanaki 40 ana gudanar da aikin, wanda ba a karbar ko sisin-kwabo hannun kowa.