Gwamnatin Jihar Legas za ta hana shan sigari
Kwanan nan gwamnati Jihar Legas za ta shiga hukunta duk wanda ta samu yana zukar tasba sigari a matattarar jama’a, domin majalisar dokokin jihar ta kammala dokar zuwa matakin karatu na 3, saboda haka ana jira Gwamna Babatunde Raji Fashola ya sa hannu.Da zarar dokar ta fara aiki, za a hana shan sigari a wurare […]
Kwanan nan gwamnati Jihar Legas za ta shiga hukunta duk wanda ta samu yana zukar tasba sigari a matattarar jama’a, domin majalisar dokokin jihar ta kammala dokar zuwa matakin karatu na 3, saboda haka ana jira Gwamna Babatunde Raji Fashola ya sa hannu.
Da zarar dokar ta fara aiki, za a hana shan sigari a wurare kamar su asibiti da tashar mota da dakunan karatu da wajen renon yara da dakunan sayar da abinci ko kuma cikin motar fasinja da dai duk wani wuri da yake matattarar jama’a ne.
Dokar za ta kunshi sassa 16, wadanda suka hada da hana sa allon sanarwa da ke tallata taba sigari, da hana sa tallar taba a kwalin tabar; haka kuma duk wuraren da aka hana shan tabar, za a sa sanarwa ba a shan taba a wannan wurin. A sashe na 4 na dokar, za a tilasta duk wani mai daya daga cikin wadannan wuraren da aka hana shan sigari, ya sa babban allon sanarwar hana shan taba, wanda rashin yin haka shi ma wani laifi ne.
Hukuncin wanda aka kama da karya wannan dokar shi ne biyan tarar Naira dubu 10 ko kuma daurin wata 1 ko kuma watanni 3 ko kuma duka biyu. Haka kuma wanda aka gurfanar kan laifin a karo na biyu, zai fuskanci tarar Naira dubu 50 ko kuma daurin watanni 3 gidan yari. Shi ma wanda ya ki sa sanarwar ba a shan taba, zai fuskaci tarar Naira dubu 100 ko kuma daurin watanni 6 a gidan yari.
Haka kuma wanda ya zuki sigari gaban karamin yaro har aka kama shi zai biya tarar Naira dubu 15 ko kuma ya yi zaman gidan yari na tsawon watanni 3, shi ma wanda ya hana jami’an tsaro ko kuma jami’i hana shan sigari cikin jama’a, ya aikata babban laifi, kuma zai fuskanci hukunci.
Dokar za ta fara aiki ne nan take da zarar gwamna ya sa mata hannu.