Gwamnatin Legas ta rarraba kayan ofis ga kungiyoyin makarantun gaba da sakandare 10
Gwamnatin Jihar Legas ta rarraba kayayyakin aikin ofis ga kungiyoyin dalibai na makarantun gaba da sakandare 10 da ke jihar, domin inganta harkokin ofisoshin kungiyoyin nasu. Makarantun su ne Jami’ar Jihar Legas da Kwalejin Ilimi ta Adeniran Ogunsanya da Kwalejin Ilimi ta Yaba da Kwalejin Ilimin Teku (Oceanography) ta Gwamnatin Tarayya da Kwalejin Gwamnatin Tarayya […]
Gwamnatin Jihar Legas ta rarraba kayayyakin aikin ofis ga kungiyoyin dalibai na makarantun gaba da sakandare 10 da ke jihar, domin inganta harkokin ofisoshin kungiyoyin nasu. Makarantun su ne Jami’ar Jihar Legas da Kwalejin Ilimi ta Adeniran Ogunsanya da Kwalejin Ilimi ta Yaba da Kwalejin Ilimin Teku (Oceanography) ta Gwamnatin Tarayya da Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Fasaha da Kwalejin Ilimin Firamare ta Micheal Otedola da kuma Kwalejin Ilimi ta St. Augustine; sai kuma Kwalejin Fasahar Lafiya ta Jihar Legas.
Kayayyakin da aka rarraba wa kungiyoyin daliban sun hada da komfutoci da injinan gurza takardu da kujerun ofis da na’urar sanyaya daki da kuma firjin. A bikin bayar da kayayyakin, kwamishinar ilmi ta jihar, Misis Olayinka Oladunjaye ta shawarci daliban su yi amfani da kayayyakin ta hanyar da ta dace, kuma su dauka tamkar kayansu ne da suka saya da kudinsu.
Ta ce gwamnati ta yi hakan ne domin daliban su samu damar tafiyar da harkokin mulkin kungiyoyinsu cikin sauki kuma ya agaza musu wajen harkokin karatunsu. Saboda haka ta bukaci kada su dauka wata toshiyar baki ce kan al’amurran gwamnati.
Da yake tofa albarkacin bakinsa, Mai baiwa gwamna shawara a hakokin ilimi, Otunba Fatai Olukoga ya ce duk da yake kayayyakin an baiwa shugabannin kungiyoyin daliban ne, sauran daliban na da damar cin gajiyarsu, illa kawai shugabannin su tabbatar ba a lalata su ba.
Da yake jawabin godiya, shugaban dalibai na makarantun gaba da sakandare na jihar, Mista Eleto Yakubu ya ce su kadai suka san irin wahalar da suke sha wajen tafiyar da harkokin mulkin kungiyoyinsu, musamman a yayin suke son aikewa da sakonni.
Haka nan ya yaba wa gwamnatin jihar kan wasu gine-gine da take yi a wasu makarantun nasu wadanda suke taimaka wa harkokin karatu.
Daga karshe ya yi fatan sauran gwamnatoci za su rika yi wa dalibai irin wannan taimakon da zai inganta iilmi sannan zai kara dankon zumunta tsakanin gwamnatoci da kungiyoyin dalibai.