Gwamnatin Legas ta taimaka wa hukumar NDLEA da motoci

Gwamnatin Jihar Legas  ta  ba da  gudunmowar  motoci  kirar  a-kori-kura  ga  hukumar  yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA)  domin ta kara azama ga aikin ta na fatattakar masu wannan mummunar sana’ar ciki da wajen Najeriya.Da yake mika motocin ga shugaban hukumar na kasa, Gwamna Babatunde Fashola ya ce gwamnatin ta yi […]

Gwamnatin Legas ta taimaka wa hukumar NDLEA da motoci

Gwamna Babatunde Fashola na Jihar LegasGwamnatin Jihar Legas  ta  ba da  gudunmowar  motoci  kirar  a-kori-kura  ga  hukumar  yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA)  domin ta kara azama ga aikin ta na fatattakar masu wannan mummunar sana’ar ciki da wajen Najeriya.
Da yake mika motocin ga shugaban hukumar na kasa, Gwamna Babatunde Fashola ya ce gwamnatin ta yi haka ne  domin ta kara wa hukumar kwarin gwiwar gudanar da ayyukanta, musamman  ganin jihar na da manyan tashoshin sufuri na duniya daban-daban.
Gwamnan ya nemi gwamnatin tarayya da kuma musamman majalisun kasa  su  samar da  hukunci mai tsanani ga masu safara da shan miyagun kwayoyi, domin  hukuncin da  ake yanke musu  ya sa da yawansu bayan an yi  musu hukuncin,  sai su sake komawa ruwa. “kasashen da suke da  hukunci mai  tsanani,  wanda  wasu  har  kashewa  ake yi, lamarin ya takaita, saboda haka idan ba a tsananta hukunci ba, to duk wani kokari da hukumar take yi zai zama ragagge”. Inji shi.
Da yake  karbar motocin,  shugaban hukumar, Alhaji Amadu Giade cewa ya yi  kalubalen da  hukumar  ke  fuskanta  a jihar  ya sha  bamban da na sauran jihohin, musamman da yake  jihar  tana  da  yawan jama’a,  wanda  karade  kowane  lungu  shi kansa  wani  babban aiki ne  duk  da hukumar  tana  da  ofisoshi  a  sassan  jihar  daban-daban.
Alhaji Giade  ya ce  bincike ya nuna akwai wani abu na musammam da jihar ke da  shi  wanda babu  a sauran jihohin, lamarin da ya sa  masu fatauci  suka  fi mayar da hankalinsu a jihar, kodayake kame  wasu  gidajen da ake sarrafa  hodar ‘mitapitamin’  wadda ta fi  hodar koken illa  ya sa sun sake wani matsugunni,  wanda  ko’ina suka shiga  cikin Najeriya za a zakulo su.
Ya ce wadannan motoci da gwamnati ta baiwa  hukumar,  za su kara mata kwarin gwiwar gudanar da ayyukanta.
Alhaji Giade ya ce tsarkake kasa daga mummunan dabi’u  nauyi ne da ke kan duk wani dan kasa nagari,  don haka  sauran jama’ar  kasa na iya sa baki wajen ganin an kara tsananta hukuncin da ake da shi yanzu kan masu fataucin.