Gwamnatin Neja za ta farfado da kulob din Neja Tornadoes
Gwamnatin Jihar Neja tana yin duk abinda ya kamata domin ganin kungiyar kwallon kafa mallakarta wato Niger Tornadoes ta koma rukunin kwararru a gasar wasa ta badi idan Allah Ya kai mu a matsayin daya daga cikin matakan da take dauka na ba wasannin motsa jiki kulawar da ta kamata. Jami’in yada labarai na kungiyar […]
Gwamnatin Jihar Neja tana yin duk abinda ya kamata domin ganin kungiyar kwallon kafa mallakarta wato Niger Tornadoes ta koma rukunin kwararru a gasar wasa ta badi idan Allah Ya kai mu a matsayin daya daga cikin matakan da take dauka na ba wasannin motsa jiki kulawar da ta kamata.
Jami’in yada labarai na kungiyar Mista George Daniya ne ya shaidawa wakilinmu haka yayin da suka yi hira da shi ta waya inda ya tabbatar cewa gwamnatin jihar ta biya duk ‘yan wasa hakkokinsu da doka da kuma ka’idar yarjejeniyar daukarsu kwantaragin da aka saba yi duk shekara kafin su yi wa kowace kungiya wasa ko kuma sabunta kwntaragi.
Mista George Daniya ya jaddada cewa ’yan kwallon Tornadoes a yanzu suna da babban buri daya ne a wannan kasar,babban burin kuwa shi ne yin wasa a rukunin wasa na kwararru da kowane dan wasa ke muradi. Duk dan wasan da ya samu haka yana da fatan samun gayyatar yi wa kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagles wasa wanda yana daya daga cikin alfaharin da cikakken ‘yan kwallo ke bugun kirji da shi.
Jami’in ya ce kwamitin da gwamnatin jihar ta kafa don kula da kungiyar yana shirye-shiryen da suka kamata domin ganin kungiyar ta koma rukunin kwararru. Ya bayyana sakacin da gwamnatin baya ta yi na rashin ba ’yan kwallon kulawar da ta dace al’amarin da ta sa suka samu koma-baya.
Jadawalin Gasar Rukunin Firimiya na Ingila a Wannan Mako:
Asabar 29 ga Agusta, 2015
Newcastle United Da Arsenal daya saura kwata na rana
Stoke City Da West Brom Uku na rana
Manchester City Da Watford Uku na rana
Liberpool Da West Ham United Uku na rana
Chelsea Da Crystal Palace Uku na rana
Bournemouth Da Leicester City Uku na rana
Aston billa Da Sunderland Uku na rana
Tottenham Da Eberton Biyar da rabi na yamma
Lahadi 30 ga Agusta, 2015
Southampton Da Norwich City daya da rabi na rana
Swansea City Da Manchester United Hudu na yamma