Hadarin mota ya kashe mutum 7 da raunata wasu a Gada-Biyu

Rahotanni na bayyana cewa, mutum bakwai sun rasu yayin da biyar suka samu mummunan rauni a wani hadarin mota da ya faru a yammacin ranar Lahadi a kauyen Gada-Biyu da ke hanyar Abuja zuwa Lokoja. Wani ganau ya shaidawa majiyarmu cewa, hadarin ya rutsa da motoci uku da wata mota kirar  Toyota hayas da ya […]

Hadarin mota ya kashe mutum 7 da raunata wasu a Gada-Biyu

Rahotanni na bayyana cewa, mutum bakwai sun rasu yayin da biyar suka samu mummunan rauni a wani hadarin mota da ya faru a yammacin ranar Lahadi a kauyen Gada-Biyu da ke hanyar Abuja zuwa Lokoja.

Wani ganau ya shaidawa majiyarmu cewa, hadarin ya rutsa da motoci uku da wata mota kirar  Toyota hayas da ya faru misalin karfe 5:23 na yamma, lokacin da wata tirela kirar Daf ta tawo a guje ta afka kan motocin.

Kwamandan Hukumar kiyaye hadurra (FRSC) na shiyyar Abaji a Abuja ACC Olasupo Esuruoso ya tabbatar da aukuwar hadarin kuma ya ce, hadarin yana da nasaba ne da yawan gudu da motocin ke yi a hanyar.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta