Hadarin mota ya yi sanadiyyar rasuwar mutum 32 a Edo – FRSC
Hukumar kiyaye hadurra ta Najeriya (FRSC) ta ce, akwai adadin mutum 32 wadanda suka rasa rayukansu a hadarin mota a jihar Edo daga watan Yuli zuwa Satumba 2018. Kwamandan hukumar reshen jihar Mr Anthony Oko ne ya sanar da hakan a wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai NAN ya yi da shi a Benin. Oko […]
Hatsarin mota
Hukumar kiyaye hadurra ta Najeriya (FRSC) ta ce, akwai adadin mutum 32 wadanda suka rasa rayukansu a hadarin mota a jihar Edo daga watan Yuli zuwa Satumba 2018.
Kwamandan hukumar reshen jihar Mr Anthony Oko ne ya sanar da hakan a wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai NAN ya yi da shi a Benin.
Oko ya ce, adadin ya hada da maza 20 da kuma mata hudu daga cikin hadurra 50 da aka yi.