‘Hadin kai shi ne babban makaminmu’

kungiyar wayar da kan ’yan Arewa mazauna jihohin Kudu maso Yamma ta kafu ne saboda gano cewa rashin hadin kai tsakaninsu yana musu babbar illa. An dade  ana tafiya yaki da su,  amma  daga  bisani  sai  a bar su da  kuturin bawa, don haka yanzu sun gane, an sha  su  sun warke, kuma sun yi […]

‘Hadin kai shi ne babban makaminmu’

kungiyar wayar da kan ’yan Arewa mazauna jihohin Kudu maso Yamma ta kafu ne saboda gano cewa rashin hadin kai tsakaninsu yana musu babbar illa. An dade  ana tafiya yaki da su,  amma  daga  bisani  sai  a bar su da  kuturin bawa, don haka yanzu sun gane, an sha  su  sun warke, kuma sun yi alwashin ba za su bi  kowa ba, sai sun tantance mazan kwarai sannan su mara musu baya.
Wasu daga cikin matsalolin da suke fuskanta, su ne korarsu da ake yi daga wuraren da suka raya da kuma rashin samar wa ’ya’yansu guraben ilmi daidai da na ’ya’yan da ke yankin, alhali baya ga masu  masaukin  nasu,  ba wata al’umma da ta yi  yawansu, amma kuma su ne  ake  warewa  a duk  lokacin  da  abin  amfanar  baki  ya zo. Kodayake  daga  cikin  manya-manyan  abubuwan da  suke  alfahari  da shi  shi ne  suna  zauna  lafiya  tsakaninsu da masu masaukin nasu.
Shugaban kungiyar,  Grema  Mohammed  Harun  ya ce  daga  lokacin  da  suka samar  da kungiyar  har  zuwa  lokacin  zabe  za su  tabbatar  duk  inda ’yan Arewa suke sun neme su sun  gana da su kuma  sun  nuna  musu  muhimmancin  hadin kai  duk da yake  siyasa ’yar ra’ayi ce  kuma  kowa  na da  damar  zaben  wanda  yake so,  amma  idan ya  tashi  zabe, akwai bukatar  ya  zabi  nagari,  wanda ke da alama yana da zuciyar son taimakon jama’a.
Shi ma  sakataren kungiya, Abdulkarim Murtala Zariya  cewa  ya yi  kuskuren  da  suka yi  a da,  ba za su  sake  yarda  su  tafka  irinsa ba,  domin shugabanninsu, musamman  sarakunan  Hausawa   su ne  suka  yi biris  suna  kallo  da  yawan  jama’ar  Arewa na shan  wahalar  da  suke  sha.  Samar da kungiyar  zai  taimaka  wajen  kawo  sauki,   domin  daga  yanzu  ba  tilas  ba ne  su bi  ra’ayin sarakunan Hausawa  a duk inda  suke  a cikin jihohin Kudu maso Yamma.
Shi ma Malam  Umar  Mohammed Azunge  da ya  wakilci  mutanen  Badun,  cewa  ya yi  wannan yunkurin yekuwar  da  suka  dauri  aniya, ba za su gaza ba domin sa kai  ya fi  bauta  ciwo,  za su  jajirce  har  sai  sun ga hakarsu  ta cimma  ruwa.  “Shi ya sa  muke  jaddada  cewa wannan kungiyar  ba ta  da nasaba  da  addini ko kabilanci ko kuma siyasa, manufarta  ita  ce  duk inda  dan Arewa  yake a Kudu  maso  Yamma,  to  ya  tabbatar  ya zabi  nagari,  wanda  zai kare  shi,  idan  bukatar  hakan  ta  taso”.  Inji shi.