Hakar mai a kogin Kolmani II zai dauke mu kwana 60 – ‘Yan kwangila
Shugaban kamfanin hakar mai na Etihad Oilfield Services Abdulrahman Bashir ya ce, aikin hakar mai da aka fara a kogin Kolmani jihar Bauchi zai iya kaiwa kwana 60 kafin a kammala shi. An fara aikin ne tare da wani kamfanin kwangila na Najeriya Messrs Etihad Oilfield Services wanda yake wani bangare ne na kamfanin AA&R […]
Shugaban kamfanin hakar mai na Etihad Oilfield Services Abdulrahman Bashir ya ce, aikin hakar mai da aka fara a kogin Kolmani jihar Bauchi zai iya kaiwa kwana 60 kafin a kammala shi.
An fara aikin ne tare da wani kamfanin kwangila na Najeriya Messrs Etihad Oilfield Services wanda yake wani bangare ne na kamfanin AA&R Investment Group da suke aikin hakar man a kogin Kolmani kusa da kauyen Barambu a karamar hukumar Alkaleri jihar Bauchi.
A ranar Asabar ne shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da fara hakkar man fetur din.