Har yanzu ina cikin aikin soja, Inji Manjo Almustafa

Wakilin Aminiya ya tattaunawa da Manjo Hamza Almustafa kan batutuwa da dama tun bayan fitowarsa  daga  gidan yari, kamar haka:AMINIYA: Ka yi watanni da  fitowa  daga  gidan yari, amma jama’a na ta  shaci-fadi kan  kana soja  ko ka bari, yaya  lamarin  yake  ne?ALMUSTAFA: Kamar  yadda  na yi  bayani, yau wata  na  5  da ’yan kwanaki […]

Har yanzu ina cikin aikin soja, Inji Manjo Almustafa
Har yanzu ina cikin aikin soja, Inji Manjo Almustafa

Wakilin Aminiya ya tattaunawa da Manjo Hamza Almustafa kan batutuwa da dama tun bayan fitowarsa  daga  gidan yari, kamar haka:
AMINIYA: Ka yi watanni da  fitowa  daga  gidan yari, amma jama’a na ta  shaci-fadi kan  kana soja  ko ka bari, yaya  lamarin  yake  ne?
ALMUSTAFA: Kamar  yadda  na yi  bayani, yau wata  na  5  da ’yan kwanaki da  fitowa, alhamdulillahi, abubuwan da ka ga ina yi, abubuwan da na  fada  ne  tun 1984, na taimaka wa matasa wajen nema  musu  ayyuka  da  makarantu  da  dai abin yi,  domin  maganin   zaman-banza, kuma ya kamata  a  taimaka musu. Batu na gaskiya shi ne Arewa  tana  neman taimako kuma  mun dade  muna  bauta mata, kuma  mu ’ya’yanta ne, don haka  za mu ci gaba da yi mata  hidima  har abada. A nan muke. A nan muka  tsaya,  kuma za mu ci gaba  da kyautata  mata.  Nauyi ne da ke kan duk  wani wanda  zai so a ce  shi da ne  nagari, kuma  taimakon,  ba  sai jiharmu ba  ko  garinmu. Wannan ne  na sa  gaba, shi kuma nake yi  a  halin yanzu.
AMINIYA: Ina batun  aikin  soja?
ALMUSTAFA: Wato  a aikin soja,  idan  aka  kai ka  kara kotu, to akwai matakai da ake dauka. Gwamnatin Jihar  Legas ta daukaka kara, sai  an  kammala  wannan  abu  ne daki-daki,  kana  hukumar  soja,  a  bisa  dokar  kasa  da  dokar  soja,  ita  kuma  ta  duba  batun  gaba daya,  kana  ta  yanke  nata  hukuncin. To  ganin  maimakon in  zauna  haka nan  shi ya sa  nake  wadannan  abubuwan  da nake  yi,  wanda  ka ce  a ji ni  nan  yau,  gobe a ji  ni  ina  can.
AMINIYA: Ana  rade-radin wai  fitowarka da hannun gwamnatin tarayya a ciki, kuma ta fidda kai ne  domin  tana  son  ta yi  amfani  da kai  saboda  cimma  manufarta ta  siyasa, me za ka ce?
ALMUSTAFA: Na ji, kuma  masu  wannan batu  ba su  da hujja. Kotu  ta  sake  ni  ne  bisa  ga  hujjar  cin  amanar  da  aka yi  mana. Kai Ladan kana nan gabanka  mai  shari’a a  kotun daukaka kara  ta share  sama da minti goma  tana karanta  abubuwan da ta  yi rantsuwa da su  da  baibul  da ta yarda  da shi  cewa  za ta  yi hukuncin  gaskiya  kuma  a kan tsoronta da Allah kan wannan batu. Shi ne  ta  karanta  hukuncin  gaban  duniya,  ta  kawo  hujjojinta  da ya sa  ta  sake ni. Wadanda  suka  azabtar  da ni  ba su  taba   tsammanin  za  a  cire  ni ba, su  sun sha yi mini  alkawarin  mutuwa,   ido-da-ido, sun  sha yi mini  alkawarin  ba  zan yi  wata  daya a raye  ba. a dake ni, a kona ni da wuta, a rataye ni. Yanzu  ba daga asibiti  nake ba? Ai naje  asibiti  kan raunukan  da  suka yi min. Daga  ni  har  iyali  har  iyaye  har ’yan uwa, ba  wanda bai azabta  ba,  daga  hannun wadannan mutnen,  ni  na ce  na yafe, idan kuma  yafewar  ce  ke  damun su a kan cewa  ba su  sani  ba,  suke ci gaba da makirce-makirce, to wannan wani  abu ne kuma daban. Ni dai  na san  ina  da  akida, kuma na san  irin  tarbiyyar  da aka yi  mini.  Kishi da tarbiyya da rikon gaskiya  da kare  kasa  ta ’yan uwa,  shi ne  abin da muka sa a gaba.
AMINIYA: Game da kalubalantar tsohon  shugaba  Obasanjo, ganin ka  taba  fadin  cewa  gwamnatin  tarayya  ta kwashe  maka wasu  bayanan  sirri, ya za ka yi abin a kaddara ya  karba bukatarka, duk da yake bai ambata sunanka ba a wasikarsa?  
ALMUSTAFA: Ba na shakka, idan a  yanzu  Obasanjo ya karba, wallahil azim,  zan yi  sujudar gode wa  Ubangiji, don na san zaman zai  haifar  da  wani  abu na  ilmantar  da  Najeriya. Zai  samar  da  wani  haske, wanda zai  taimaka wa na kasa, kuma  zai  taimaki  Najeriyan  kwarai  da  gaske.  Maganar  kwashe  kayana,  wannan  gaskiya  ne,  lokacin   da  aka  kama  ni,  duk   abubuwan  da nake  da su,  an kwashe, ba ni  da  komai  banda  kayan  da ke  jikina, amma  maganar  wasu  hujjoji,  a  ko’ina  suke  a duniya,  wannan  wani  abu  ne wanda   yake  sirrina ne. Kai  ka  bari ka gani, ka  taya ni addu’a  Allah Ya sa  ya  amince  cewa  ni da shi  za mu  zauna  mu yi  magana  a kan  abubuwan da  suka  addabi   wannan  kasar. Nan  za ka  fahimci  me  nake  nufi. Game da kiran suna, ai da ya kira sunana da  ka ji  irin martanin da  zan bayar, amma  tunda  bai kira  sunana  ba,  shi ya sa  nake kalubalantarsa. Ba  cika  baki ba, ni  ba irin mutanen nan ba ne  masu  fankama, ko  girman  kai,  a’a, idan  gaskiya  ta  tashi  fitowa  dole  karya  ta  kauce,  kuma  za mu yi  shi  ne  cikin ladabi  da biyayya.
AMINIYA: Daga abin da na fahimta  da kai, ka san harkokin tsaron kasar nan, yanzu  idan gwamnatin  tarayya  ta bukace ka kan wannan bangare za ka amsa?
ALMUSTAFA: Abin da  ka ga  zai  cutar da Najeriya da abin da kuma za ka yi  wajen taimaka wa  al’umma, cikin  tsoron  Allah,  cikin  gaskiya,  to  dukkan  da  nagari,  bai  kamata  ya  guje  shi ba. To in  sun kira ni, dayake kowane abu yana da tashi hujjar (sharadi), zan ba da  hujjojina (sharuddana) na yin aikin,  idan  sun amince, sai na yi  idan  kuma  ba su  amince  ba,  sai  a  daina. Ni  ba na  yin  abu  kan  munafunci  ko kuma  take  gaskiya ko kuma  wulakanta  mutane, ko  kuma  cutar  da  mutane, bai yiwu ba  a da,  kuma  ba  zai  yiwu ba a yanzu.
AMINIYA: Yaya batun kiraye-kirayen jama’a na ka shiga  siyasa, mene ne  ra’ayinka?
ALMUSTAFA: kwarai  da  gaske  suna  ci  gaba  da  wannan kiran. Na  tafi  Kaduna  da Jos  wajen  da  aka yi  fadace-fadace, domin  taimakonsu da  gyaran  masallatansu  da  makarantunsu  da  wajen  ba su   abinci  da magani, mutane  da  yawa  a  wadannan  wuraren  suna  ta  wadannan kiraye-kirayen, amma ni wannan bai  shiga  hankali  na ba tukunna. Arewar da  sani  kafin a  daure  ni  da  Arewar  da nake  gani yanzu  ta  canza, abin da  nake  fata  shi ne  Allah  Ya  kawo  wa kasar  nan dauki  da taimako  ga  talaka. Duk  wadannan  shugabannin matasan da kake gani nan  sun zo  ne daga  sassan  kasar  nan daban-daban, a kan yadda  za mu  taimaki  matasa,  kuma  muna  nan muna yi.  Yanzu  haka  mun  hada  hannu  da  wani  mai  gonar  kaji,  dan kasar  Kenya, matasa  dubu 10  ne  za a  samar wa  aikin yi  na  kiwon  kaji, a sassan  kasar  nan daban-daban.