Hatsarin kwalekwale ya ci rayuka 4 a Borno

Akalla mutane hudu sakamakon kifewar wani kwalekwale a Karamar Hukumar Dikwa da ke Jihar Borno

Hatsarin kwalekwale ya ci rayuka 4 a Borno

Yadda masu kwalekwale ke tsallakar da fasinjoji

An tabbar da rasuwar akalla mutane hudu sakamakon kifewar wani kwalekwale a Karamar Hukumar Dikwa da ke Jihar Borno.

Kakakin ’yan sanda a jihar, ASP Kenneth Daso, ya sanar a ranar Talata, cewa “hatsarin kwale-kwale ya afku a ranar 23 ga watan Satumba, 2024 a yankin Bakassi da ke tsakanin Mafa da Dikwa a kan hanyar Maiduguri, inda ya yi sanadin asarar rayukan mata hudu.

“Wadanda suka mutu, dukkansu ’yan unguwar Bulabulin, Dikwa, kuma an gano su, an kai su babban asibitin Dikwa, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarsu.

“Daga bisani an mika gawarwakin ga iyalansu domin yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.”

Kwamishinan ’yan sandan jihar, ML Yusufu, a yayin jajantawa, ya bukaci mazauna yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa, da su yi taka-tsan-tsan a wannan lokaci, tare da gaggauta kai rahoton duk wani lamari na gaggawa.

Ambaliya: Binani ta bai wa Maiduguri tallafin 50m

An sallami sojar da ta zargi shugabanta da neman lalata da ita

CBN ya ƙara kason kuɗin ruwa zuwa 27.25 cikin 100

Hatsarin kwalekwale ya ci rayuka 4 a Borno