Hatsarin mota ya kashe mutum 12 a Zamfara

Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa FRSC ta alakanta aukuwar hatsarin da tukin ganganci.

Hatsarin mota ya kashe mutum 12 a Zamfara

Akalla mutum 12 ne ajali ya katsewa hanzari ciki har da yara biyu sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da su a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.

Lamarin, kamar yadda wani ganau ya shaida wa wakilinmu, ya ce ya faru ne da misalin ƙarfe 1:20 na rana a kan babbar hanyar Funtuwa zuwa Tsafe.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, hatsarin ya rutsa da mutum 24 — 22 a cikin wata motar haya da wasu mutum biyu a wata A Kori Kura kirar Toyota.

Hatsarin wanda ya auku a sakamakon tsautsayi, bayanai sun ce an yi taho-mu-gama ne tsakanin motocin yayin da gudanarwar motar hayar ta kwace daga hannun direbanta.

Yanzu haka dai an kwantar da wadanda suka jikkata a Babban Asibitin Tsafe, inda suke karɓar magani.

Wani jami’in Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) da ya bukaci a sakaya sunansa, ya alakanta aukuwar hatsarin da tukin ganganci.

“Ina cikin jami’an FRSC da suka kai dauki wurin da hatsarin ya faru wanda ya rusta da mutum 24 a duk motocin biyu.

“Wadanda suka mutu sun hada wasu mutum 10 da kananan yara biyu, yayin da kuma da dama suka jikkata,” a cewarsa.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan