Hawan Daushe: Yadda Sarkin Zazzau ya karɓi gaisuwar sallah

Sarkin ya karɓi gaisuwar sallah ne a ranar hawan Daushe a Zariya.

Hawan Daushe: Yadda Sarkin Zazzau ya karɓi gaisuwar sallah

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ahmad Nuhu Bamalli, ya karɓi gaisuwar sallah daga baƙi daga ciki da wajen ƙasar nan a lokacin bikin hawan Daushe a Zariya.

Sarkin ya karɓi gaisuwar sallah a fadarsa da ke Zariya, inda ya yi wa ɗaukacin al’ummar Musulmi fatan alheri da kuma fatan Allah Ya karɓi ibadansu.

Kazalika, Sarkin ya yi kira ga shugabanni da su tashi tsaye wajen magance matsalar ’yan fashin daji da ke yin garkuwa da mutane.

Ga hotunan yadda Sarkin ya karɓi gaisuwar sallah daga baƙi:

Ango ya kashe amaryarsa da wuƙa har lahira

Obi ya girmi Kwankwaso a fagen siyasa — Bashir Ahmad

Gobara ta yi ajalin wani mutum yayin da yake barci a gidansa

Da jami’an gwamnati nake zuwa tattaunawa da ’yan bindiga – Gumi