Hezbollah ta kai hari hedikwatar leken asirin Isra’ila

Isra’ila ta yi ikirarin kakkabo makami mai linzami da aka harbo daga Lebanon

Hezbollah ta kai hari hedikwatar leken asirin Isra’ila

Kungiyar Hezbollah da ke kasar Lebanon ta ce mayakanta sun harba makamin roka kan hedkwatar hukumar leken asirin Isra’ila ta Mossad da ke kusa da birnin Tel Aviv a ranar Laraba.

Rundunar sojin Isra’ila ta yi ikirarin kakkabo wani makami mai linzami da Hezbollah ta harbo daga Lebanon.

An yi ta jin karar jiniyar gargadi a Tel Aviv, cibiyar tattalin arzikin Isra’ila, amma babu labarin ko an samu asarar rayuka ko jikkata.

An kuma kara jin karar gargadi a wasu yankuna na tsakiyar Isra’ila, ciki har da birnin Netanya.

Kakakin rundunar sojin Isra’ila Nadav Shoshani ya ce ba zai iya tabbatar da manufar Hizbullah da harba makami mai linzami daga Lebanon.

A wannan mako ne sojojin Isra’ila sun kai hare-hare mafi muni a cikin shekara guda da ake gwabzawa.

Sun kai hari kan shugabannin kungiyar Hizbullah da ke samun goyon bayan kasar Iran da wasu daruruwan wurare a cikin kasar Lebanon.

Isra’ila kuma ta sake kai hare-hare ta sama a kudancin Labanon a kazamin fada mafi muni tsakaninsu a cikin shekara guda.

TY Danjuma Ya Bayar da Tallafin N1bn Kan Ambaliyar Maiduguri

Hezbollah ta kai hari hedikwatar leken asirin Isra’ila

MDD ta gaza ɗaukar mataki kan yaƙin Gaza —Erdogan

Duk da man Dangote, wahalar fetur ta dawo a Abuja