Hizbullah ta kai wa sojojin Isra’ila harin bom

Ƙungiyar Hizbullah ta ce mayaƙanta sun kai wa sojojin Isra’ila harin bom a wani kauye da ke Kudancin kasar Lebanon a safiyar Litinin.

Hizbullah ta kai wa sojojin Isra’ila harin bom

CORRECTS DATE TO MONDAY, OCT. 7, FROM SUNDAY, OCT. 6 – Flames and smoke rise from an Israeli airstrike in Dahiyeh, Beirut, Lebanon, Monday, Oct. 7, 2024. (AP Photo/Bilal Hussein)

Ƙungiyar Hizbullah ta ce mayaƙanta sun kai wa sojojin Isra’ila harin bom a wani kauye da ke Kudancin kasar Lebanon a safiyar Litinin.

Hakan na zuwa ne bayan Isra’ila ta sanar da tura ƙarin rundunar sojojinta domin aiwatar da yaƙinta da Hizbullah a Lebanon.

Ƙungiyar, wadda ta lashi takobin ci ba da yakar Isra’ila, ta ƙara da cewa, mayaƙanta “sun yi wa taron sojojin Isra’ila luguden bama-bamai a dandalin Maroun al-Ras.”

Ta fitar da wannan sanarwar ce bayan da farko ta ce mayaƙanta sun kai wasu hare-hare na daban kan sojojin Isra’ila a kan iyakar ƙasar Lebanon.

 

AFP.

Mahara sun ƙona Sakatariyar Karamar Hukuma bayan janyewar ’yan sanda

Hizbullah ta kai wa sojojin Isra’ila harin bom

Hamas ce da nasara a kan Isra’ila —Khalid Masha’al

Za a yi facin titin Abuja zuwa Tafa a kan miliyan N366