HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano
Duk da bincike ya soma gudana, amma kawo yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.

Wata gobara da ta auku safiyar wannan Larabar ta laƙume kasuwar ’yan gwan-gwan da ke unguwar Dakata a Ƙaramar Hukumar Nassarawa ta Jihar Kano.
Kasuwar wadda ake kira da Kwalema tana nan a kan titin Zango, daura da gidajen man Dominion da kuma Mobil da ke makwabtaka da ofishin Hukumar WAEC.
- Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi
- DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna
Mai magana da yawun hukumar kwana-kwana Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa jami’ansu na ci gaba da ƙoƙarin kashe gobarar da ke neman wuce gona da iri.
Sai dai ya bayyana cewa duk da bincike ya soma gudana, amma kawo yanzu ba su gano musabbabin tashin gobarar ba.