Hotuna: Asari Dokubo ya ziyarci Ganduje a Abuja

Asari ya ziyarci Ganduje don taya murnar zama shugaban jam’iyyar APC na kasa.

Hotuna: Asari Dokubo ya ziyarci Ganduje a Abuja

Dakubo da Ganduje

Tsogon Jagoran Tsagerun Neja Delta, Asari Dokubo, ya kai ziyarar taya murna ga shugaban jam’iyyar APC na Kasa, Abdullahi Umar Ganduje a Abuja.

Dokubo ya taya Ganduje murnar zama shugaban jam’iyya mai mulki ta kasa.

A wani sako da ta wallafa a shafin X (Twitter), jam’iyyar mai mulki ta ce tsohon gwamnan Kano, ya karbi bakuncin dan gwagwarmayar a gidansa da ke babban birnin tarayya, Abuja.

“Shugaba Abdullahi Umar Ganduje, ya karbi bakuncin Tsohon Jagoran Masu Tayar da Kayar Baya a Neja Delta, Asari Dokubo, a wata ziyarar taya murna a gidansa da ke Abuja,” in ji jam’iyyar.

Ga hotunan ziyarar a kasa:

Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn

Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

An ga watan Ramadan a Najeriya

Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki