HOTUNA: Gini ya kashe mai ‘dibar ganima’ a Kano

Har yanzu akwai mutum biyu da ake zargin suna cikin ginin

HOTUNA: Gini ya kashe mai ‘dibar ganima’ a Kano

Masu dibar ganima

Gini ya danne mutane da dama da ake zargin masu dibar ganimar rodina da saura kayan gini ne a tsohon otal din Daula da ke Kano.

Ginin dai na daya daga cikin wadanda Gwamnatin Jihar Kano ta rusa bisa dalilin cewa tana kokarin kwato filayen gwamnati da aka cefanar ba bisa ka’ida ba.

Rahotanni sun tabbatar da cewa mutum daya ya rasa ransa, wasu uku kuma an ceto su da rai, wasu kuma har yanzu ana ci gaba da aikin ceto su.

Shaidun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne wajen misalin karfe 2:30 na rana, lokacin da mutanen ke kokarin dibar rodi daga cikin ginin.

Kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusuf, wanda ya yi magana da wakilinmu a wajen, ya ce yanzu haka jami’ansu sun sami nasarar ceto mutum uku da ransu.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoton, ana zargin akwai karin wasu mutum biyu ko fiya da haka a cikin ginin.

Ga wasu daga cikin hotunan aikin ceton:

Masu dibar ganima

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan