HOTUNA: Yadda Shettima ya kaddamar da bude Masallacin Majalisar Wakilai

Shettima ya ja hankalin shugabanni wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

HOTUNA: Yadda Shettima ya kaddamar da bude Masallacin Majalisar Wakilai

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya kaddamar da Masallacin Juma’a da al’ummar Musulmi suka gina a majalisar dokoki.

Aminiya ta ruwaito cewa, Shettima ne ya wakilci Shugaban Kasa Bola Tinubu a wajen taron bude Masallacin.

Da yake jawabi, mataimakin shugaban kasar, ya ce, ya je bude Masallacin ne don taya al’ummar Musulmi murna a Majalisar Dokokin.

Ya kuma yi kira ga shugabanni da su kasance masu tawali’u yayin da suke sauke nauyin da aka dora musu a lokacin da suke rike da madafun iko da kuma neman lahirarsu ta hanyar samar da irin wadannan ayyuka da kuma sadaka.

Ga hotunan a kasa:

An gurfanar da wanda ya kashe matarsa da ƙona gida

Atiku ya caccaki Tinubu kan rikicin BCDA

An kama ’yan Togo biyu kan shirin garkuwa da mutum

’Yan bindiga sun sace ’yan gudun hijira a Sakkwato