Hukumar NDLEA ta cafke masu fiton kaya
Hukumar yaki da safarar miyagun kwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kame wasu mutane da ke fiton kayayyaki a tashar jirgin saman na kasa-da-kasa da ke Legas da miyagun kwayoyi. Cikin kayan har da tabar wiwi da kuma hodar ‘mefitamin’, wanda nauyinsu ya kai kilogiram 55.6. An boye su cikin kayan abinci da kuma gashin da […]
Hukumar yaki da safarar miyagun kwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kame wasu mutane da ke fiton kayayyaki a tashar jirgin saman na kasa-da-kasa da ke Legas da miyagun kwayoyi.
Cikin kayan har da tabar wiwi da kuma hodar ‘mefitamin’, wanda nauyinsu ya kai kilogiram 55.6. An boye su cikin kayan abinci da kuma gashin da mata ke amfani da shi wajen kitso. An cafke wannan mummunar hajar ce a lokacin da suke kokarin shiga jirgi zuwa kasar Sin da kuma Afirka ta Kudu.
Da yake wa taron manema labarai jawabi, shugaban hukumar, mai kula da tashar jirgin saman Murtala Mohammed, Malam Hamza Umar ya ce wannan kamun shi ne irinsa na farko da ya fi yawan adadin kayan tun farkon wannan shekarar.
daya daga cikin wadanda aka kama, wanda dan asalin Jihar Anambra ne, dan kasuwa mazaunin kasar Guinea, mai suna Sylbester Nmadi Augustine, amma da fasfon kasar Guinea da ke da sunan Keita Mamady ya ce an umurce shi ne da ya kai kwayar Hong Kong kana ya wuce Guangzhou, inda za a biya shi ladar wannan aikin nasa.
Mutun na biyu mai suna Samuel Williams ya shaida wa manema labarai cewa abokinsa ne da ke zaune a Afirka Ta Kudu ya nemi ya sawo masa gashin mata da ake karawa wajen kitso. “Da aka kawo, sai na ba masu aikewa da kaya kasar waje, ashe wadanda suka kawo gashin sun boye miyagun kwayoyi ciki, ni ban sani ba”, inji shi.
Mutumi na 3, dan asalin Jihar Ogun, mai suna Adams Adewumi ya ce abokin aikinsa ne Samuel ya ba shi sundukin don ya kai masa cikin jirgi mai tafiya kasar Afirka ta Kudu, amma bai fadda masa akwai wannan mugunyar hajar ba, sai da jami’an hukumar ta NDLE suka gano ashe an boye ta a ciki, kuma shi Samuel bai musanta shi ya aike shi ba.
Shugaban hukumar ya ce da zaran sun kammala bincike za su gurfanar da wadanda ake tuhumar a kotu.