Hukumar NDLEA ta kame wata mata da hodar iblis
Hukumar yaki da sha da safaran miyagun kwayoyi (NDLEA) da ke Ikko ta cafke wata mata mai suna A’isha Uwaminana, wadda ta ce ta fito ne daga kasar Burundi ta shigo jirgin AIR REWANE daga kasar Tanzaniya kuma ta iso nan Najeriya kafin saurayinta dan Najeriya da ta ce ya ba ta jikkar da ke […]
Hukumar yaki da sha da safaran miyagun kwayoyi (NDLEA) da ke Ikko ta cafke wata mata mai suna A’isha Uwaminana, wadda ta ce ta fito ne daga kasar Burundi ta shigo jirgin AIR REWANE daga kasar Tanzaniya kuma ta iso nan Najeriya kafin saurayinta dan Najeriya da ta ce ya ba ta jikkar da ke dauke da wannan mugunyar hajar ya iso.
Hodar ta iblis, wadda ke kunshe cikin jikkarta ta kaya, ta ce saurayinta ne ya ba ta kafin ya iso nan Najeriya, inda za su zo domin bikin aurensu. Ta ce ta hadu da wannan dan talikin ne can kasarsu kuma sun yi alkawarin yin aure abin da ya sa ya fara turo ta zuwa Najeriya kafin shi ya iso, ta fara shirye-shiryen bikin auren nasu, sai dai ta ce ba ta da masaniyar cewa akwai wannan hodar kunshe cikin wannan jikkar.
Kamar yadda shugaban hukumar mai kula da tashar jirgin saman Murtala Mohammed, Malam Hamza Umar ya shaida wa wakilin Aminiya, jirgin da matar ta shigo ba jirgi ne da aka saba samun mutane dauke da wannan hodar iblis din. Ya ce yana ganin shigar ta jirgin wata dabara ce ta dauke hankalin jami’an hukumar domin ganin kila ba za a yi wa fasinja binciken kwakwaf ba, amma ba ta san cewa kowane jirgi ko fasinja sai an yi masa binciken da ya dace.
Ya ce ba ita kadai ce ’yar kasan waje da ke hannun hukumar ba a yanzu haka, domin akwai wasu biyar ’yan kasashe biyar da hukumar ta kame cikin wannan shekarar a lokutta daban-daban kuma akwai wasu ukku daban wadanda su har an yanke musu hukunci har sun fara zaman gidan kaso. Ya ce da zarar sun kammala binciken wannan matar za su gurfanar da ita gaban kuliya.
Matar ta ce wannan shi ne karo na farko da ta zo Najeriya. Kamun matar ce a tashar jirgin saman Murtala ya zo daidai da lokacin da wasu jami’an kasar Switzerland masu yaki da harkoki da miyagun kwayoyi na kasarsu suka zo domin duba hanyoyin da kasar tasu za ta hada kai da Najeriya domin yakar wannan mummunar sana’ar tsakanin kasashen biyu da ma duniya baki daya.
Da yake wa bakin nasa marhabin, shugaban hukumar NDLEA na kasa, Alhaji Ahmadu Giade ya ce duk da damke masu wannan mummunar sana’ar da hukumar ke yi har yanzu wasu ba su daddara ba. Ya yi fata za su yi kyakkyawar musayar ra’ayi da bakin, wanda zai amfani kasashen biyu da ma sauran kasashen duniya.Ba a yi bayanin kowane tsawon lokaci bakin jami’an za su yi a nan Najeriya ba.