Hukumar NDLEA ta yi kamun farko a tashar jirgin saman Inugu
Ba a fi wata guda ba da fara aiki da sabuwar tashar jirgin sama ta Akanu Ibiam da ke Inugu ba, a matsayin filin jirgin saman kasa da kasa ba, Hukumar Yaki da Safarar Miyagun kwayoyi da Safararsu ta kasa (NDLEA) ta yi kamun farko na wani wanda ya ce shi dalibi ne da hodar […]
Ba a fi wata guda ba da fara aiki da sabuwar tashar jirgin sama ta Akanu Ibiam da ke Inugu ba, a matsayin filin jirgin saman kasa da kasa ba, Hukumar Yaki da Safarar Miyagun kwayoyi da Safararsu ta kasa (NDLEA) ta yi kamun farko na wani wanda ya ce shi dalibi ne da hodar koken ta miliyoyin Naira.
dalibin mai suna Chizoba Anselem, wanda ya ce yana Jami’ar Nnamdi Azikwe ne da ke garin Okar, an kama shi ne a hanyarsa ta zuwa kasar Birazil sa’ilin da zai shiga jirgin kamfanin Ethiopia, wanda zai yada zango a Dubai, bayan ya hadiye kullin koken 25 da aka nannade cikin kororon roba.
Da yake wa manema labarai jawabi, shugaban hukumar na Inugu, Mista Nsikak Abasi ya ce koken din na da nauyin kilogiram 1.25, wanda ke da kimar miliyoyin Naira kuma wanda ake tuhumar bai musa ba, ya ce an yi masa alkawarin Naira dubu dari 5 ne.
Shi kuma Francis Bawaba, wanda ke zaune a Madrid na kasar Spain an kama shi da koken, wadda nauyinta kilogiram 6.490 ne, wadda kumaaka kiyasta kudinta ya kai Naira miliyan 72 kuma za a ba shi ladar Naira miliyan 3.3.
Shugaban hukumar, mai kula da tashar jirgin saman Murtala, Malam Hamza Umar ya shaida wa manema labarai cewa da zarar sun kammala bincike za su gurfanar da wanda ake zargin gaban kotu.