Ina da nasaba da Najeriya —Gimbiya Meghan
Gimbiya Meghan Markle da Yarima Harry sun ziyarci wasu kasashen Afirka a bana.
Gimbiya Meghan Markle da Yarima Harry
Sirikar Sarki Charles III, Meghan Markle ta ce wani bincike da ta gudanar ya tabbatar mata da cewa tana da nasaba da Najeriya ta wajen kakanni.
Uwar gidan Yarima Harry a wata hira ta musamman da ta yi da Spotify, ta ce binciken kwayoyin halitta da aka mata shekaru da suka gabata, an tabbatar mata da cewa tana da jinin Najeriya a jikinta da kusan kashi 43 cikin 100.
- NDLEA ta cafke dillalan miyagun kwayoyi 192 a Ebonyi
- Sarki Charles III ya tabbatar Rishi Sunak a matsayin Firaministan Birtaniya
Sai dai ko da aka tambaye ta daga wacce kabila take a Najeriyar, ta ce bata da masaniya a kai, amma za ta fara bincikawa nan ba da jimawa ba.
A baya-bayan nan ne dai Gimbiya Meghan ta bayyana cewa tana da jini biyu a jikinta, amma ba ta yi cikakken bayan kan asalin nata ba.
A shekarar 2015 ne Mujallar ELLE ta wallafa labarin Gimbiya Meghan game da asalinta na ruwa biyu.
A watan Satumba na 2019, Gimbiyar ta yi jawabi ga asalinta na launin fata a karon farko tun lokacin da ta auri Duke na Sussex.
A cewar RFI, ma’auratan sun ziyarci wasu kasashen Afirka a wannan shekarar.