Ina gaskiyar musuluntar ’yar fim Lizzy Anjorin?
A farkon makon da ya gabata ne labarai suka cika kafafen watsa labaran ’yan fim, cewa ’yar fim din nan da ake kira da sunan Lizzy Anjorin ta karbi Musulunci, har ma ta canza suna zuwa A’isha.Kamar yadda binciken Aminiya ya tabbatar, ya zuwa rubuta labarin nan dai ba a samo hakikanin dalilin musuluntar ’yar […]

A farkon makon da ya gabata ne labarai suka cika kafafen watsa labaran ’yan fim, cewa ’yar fim din nan da ake kira da sunan Lizzy Anjorin ta karbi Musulunci, har ma ta canza suna zuwa A’isha.
Kamar yadda binciken Aminiya ya tabbatar, ya zuwa rubuta labarin nan dai ba a samo hakikanin dalilin musuluntar ’yar fim din ba, duk da cewa wata kafa ta bayyana cewa ana zaton wani saurayinta ne da suke shirin aure ya ja ra’ayinta ta amshi Musuluncin, kasancewar shi ma Musulmi ne.
Lizzy ta dade tana fitowa a fina-finan Najeriya na Ingilishi da kuma na Yarabanci, kuma a iya cewa dai ta samu nasara, domin kuwa a halin yanzu ma ta kusa kammala shirya fim din kashin kanta, wanda aka kashe kudi masu yawa wajen shirya shi. Fim din wanda ke kusa da fitowa, mai suna ‘Kofo De First Lady,’ an ce zai kayatar.
Haka kuma, an samu bayanin cewa, a kwanakin baya ne Lizzy (A’isha) ta yi ta zirga-zirga tsakanin kasashen Indiya da Marokko da Kamaru da sauran kasashe daban-daban, inda ta rika safarar suturu, tana dankare sabon shagonta na sayar da suturu mai suna ‘Pick Me Reloaded’ a Legas.
Kamar yadda jaridar da ake bugawa a intanet, ‘Osun Defender’ ta bayyana, ’yar wasan dai an haife ta ne a unguwar Badagry, Legas kuma tana da ‘ya daya. Haka kuma, a zancen da ake yi, A’isha (Lizzy), tana Makka, inda take sauke farali, babbar alamar da ke kara tabbatar da gaskiyar cewa lallai ta musulunta.