Ina neman yafiyar magoya bayan Arsenal kan shan kaye a hannun Brighton —Arteta

Arteta ya ce abu ne mai yiwuwa Arsenal ta lashe Firimiyar Ingila ta bana.

Ina neman yafiyar magoya bayan Arsenal kan shan kaye a hannun Brighton —Arteta

Kociyan Arsenal, Mikel Arteta, ya nemi afuwar magoya baya dangane da shan kayen da kungiyar ta yi har gida a hannun Brighton da kwallaye 3 da nema a ranar Lahadi.

Rashin nasarar da Arsenal ta yi ya sa kungiyar ta barar da damarta ta karshe a rige-rigen lashe kofin Firimiyar Ingila tsakaninta da Manchester City.

Gunners dai ta shafe tsawon lokaci tana jagorancin teburin gasar ta Firimiya, a kokarin kawo karshen dakon shekaru 19 da ta yi a baya don kai kofin gida.

To sai dai Arsenal wadda ta lashe Kofin har sau 11 a tarihi, ta gamu da gagarumin matsin lamba a watannin baya-bayan nan daga City.

Wasanni 2 cikin 7 da Arsenal ta doka a baya-bayan nan kadai ta iya samun nasara, wanda ke nuna yiwuwar bankwananta da kofin na Firimiya daidai lokacin da ake da tazarar maki 4 tsakaninta da City, kuma tawagar ta Guardiola ke da wasa guda a hannu.

A jawabinsa gaban manema labarai Arteta ya ce salon wasan da Arsenal ta yi a zagaye na biyu na haduwar ta jiya sam ba abin karba ba ne.

A cewarsa a lissafe, iya lashe kofin na Firimiya ga Arsenal har yanzu abu ne mai yiwuwa amma a yanzu abin da ya fi muhimmanci garesu shi ne samar da gyara ga kura-kuren da suka yi a jiya.

Idan har Arsenal ta gaza nasara a haduwarta da Nottingham Forest a lahadi mai zuwa, kuma City ta yi nasara kan Chelsea a ranar 21 ga watan nan, kai tsaye tawagar ta Pep Guardiola ta lashe kofin karo na 5 cikin shekaru shida.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan