Iran ta zargi Ukraine da kai hari kan jirgin ruwanta a Tekun Caspian
Iran ta ce harin ya yi sanadin mutuwar wani ma’aikacin jirgin ruwa guda, yayin da wani ya samu raunuka.
Ƙasar Iran ta bayyana rashin jin daɗinta kan yadda Ukraine ta kai wa wani jirgin ruwanta hari a Tekun Caspian.
A cewar hukumomin Iran, harin ya yi sanadin mutuwar wani ma’aikacin jirgin ruwa guda, yayin da wani ya samu raunuka.
- Mataimakiyar Shugabar Mata ta APC a Yobe ta rasu
- Jigawa ce jiha ta biyu mafi nagartar mulki a Najeriya — Rahoto
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta ce ta miƙa wa jami’an Ukraine takardar ƙorafi kan lamarin, tana mai bayyana harin a matsayin abin da ya saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa.
Sai dai har zuwa lokacin fitar wannan rahoto, Ukraine ba ta fitar da wata sanarwa da ta tabbatar ko ta musanta zargin da Iran ta yi.