Isra’ila ta ɗaiɗaita yara sama da 400,000 a Lebanon — UNICEF

UNICEF ta ce yaƙin ya hana gomman yara zuwa makaranta da kuma raba su da muhallansu.

Isra’ila ta ɗaiɗaita yara sama da 400,000 a Lebanon — UNICEF

Asusun Tallafa wa Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF), ya bayyana cewa akwai ƙananan yara sama da 400,000 da Isra’ila ta ɗaiɗaita a Lebanon, ta hanyar hare-hare ciki mako uku.

A daidai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare a Lebanon da sunan yaƙi da dakarun Hezbollah, UNICEF ta ce rayuwar dubban ƙananan yara na ci gaba da faɗawa cikin hatsari.

Asusun ya ce hare-haren sun tilasta wa yaran barin matsugunansu don tsira da rayukansu.

Mataimakin Babban Daraktan UNICEF a ɓangaren ayyukan jin-ƙai Ted Chaiban, ya yi gargaɗin cewa wannan yaƙi da Isra’ila ta faro a Lebanon kai-tsaye ya lalata tsarin ilimin ƙasar bayan da ya tilasta wa yara aƙalla miliyan 1.2 barin makarantu.

A cewar jami’in galibin makarantun da ke wannan yanki sun fuskanci hare-hare daga Isra’ila wanda ko dai ya lalata su ta yadda ba za a iya karatu ba ko kuma ya firgita yaran da ke yankin.

UNICEF ta ce akwai aƙalla asibitoci 12 da hare-haren Isra’ilar ya shafa a yankin na kudancin Lebanon mai iyaka da Isra’ila wanda ya jefa rayuwar gomman ƙananan yara cikin hatsari.

Kawo yanzu sama da mutum 2,300 ne Isra’ila ta kashe a hare-haren da ta ke kai wa Lebanon da kaso mai yawa na mata da ƙananan yara.

Cutar Kwalara ta kashe mutane 45 a Kano

Rikicin PDP: Gwamnoni sun ba Damagum wa’adin yin murabus

DAGA LARABA: Me Ya Sa Kimar Dattawa Ta Ragu A Cikin Al’umma?

Abba ya yi tafiya yayin da rikici ya dabaibaye NNPP a Kano