Jagoran yaki da zaluncin turawa a Afirka ta Kudu ya rasu

Shugaba a kabilar Zulu kuma jagoran yaki da wariyar launin fata a kasar Afirka ta Kudu, Mangosuthu Buthelezi, ya rasu yana da shekaru 95.

Jagoran yaki da zaluncin turawa a Afirka ta Kudu ya rasu

Mangosuthu Buthelezi Mangosuthu Buthelezi ya rasu ranar Asabar 9 ga Satumba, 2023 yana da shekaru 95.(Tsohon hota: Rajesh Jantilal / AFP).

Jagoran yaki da wariyar launin fata a kasar Afirka ta Kudu kuma shugaba a kabilar Zulu, Mangosuthu Buthelezi, ya rasu a safiyar Asabar yana da shekaru 95.

Shugaban kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ne ya sanar da rasuwar Mangosuthu Buthelezi, dan gwagwarmayar da ya jagoranci boren bakaken fatar a Afirka ta Kudu da ya kawo karshen mulkin danniya da turawan mulkin mallaka a kasar a shekarar 1994.
“Na kadu da rasuwar YarimA Mangosuthu Buthelezi … Firaministan Masarautar Zulu da ma kasa baki daya, wanda shi ne uban jam’iyyar Inkatha Freedom Party.”Yarima Mangosuthu Buthelezi jagora ne abin koyi a fannin siyasa da raya al’adun kasarmu, musamman wajen gwagwarmayar samun ’yancin kai a 1994 da kuma kafuwar dikomuradiyya,” in ji Shugaba Ramaphosa.Buthelezi babban basarake ne a kabilar Zulu, wadda ita ce kabila mafi yawan al’umma a kasar Afirka ta Kudu.Shi ne kuma Firaministan garin kabilar, wato KwaZulu, kuma wanda ya assasa jam’iyyar Inkatha Freedom Party, ta ’yan kabilar Zulu.

An kama matashi ɗauke da hannun mutum da bindigogi

NDLEA ta kama miyagun ƙwayoyi tan 3.9 da kama mutum 599

An kashe ’yan gudun hijira uku a Sakkwato

Kotu ta soke hukuncin yi wa Jam’iyyar NDC rijista